Mace ta zama shugabar masu rinjayen majalisar dokokin Adamawa

0
102
adamawa-house-of-assembly
adamawa-house-of-assembly

Kakakin majalisar dokokin Jihar Adamawa, Honarabul Bathiya Wesley, ya nada Kate Raymond Mamuno, a matsayin shugabar masu rinjayen majalisar.

Wesley, ya sanar da haka ne a zaman majalisar na ranar Litinin, ya kuma bayyana dan majalisa mai wakiltar karamar hukumar Maiha Jingi Belel, a matsayin mataimakin shugaban masu rinjayen.

Haka kuma kakakin majalisar ya bayyana mamba mai wakiltar karamar hukumar Yola ta Arewa, Suleiman Umar Alkali, a matsayin shugaban marasa rinjayen majalisar ta takwas.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here